37.Those drawn up in Ranks

  1. Inã rantsuwa da mãsu yin sahu-sahu (a cikin salla kõ yãƙi)
  2. Sa'an nan mãsu yin tsãwa* dõmin gargaɗi
  3. Sa'an nan da mãsu karãtun abin tunãtarwa
  4. Lalle Abin bautawarku haƙĩƙa ¦aya ne
  5. Ubangijin sammai da ƙasã da abin da ke tsakãninsu, kuma Ubangijin wurãren fitar rãnã
  6. Lalle Mũ, Mun ƙãwatãr da sama ta kusa da wata ƙawa, watau taurãri
  7. Kuma sunã tsari daga dukan Shaiɗan mai tsaurin kai
  8. Bã zã su iya saurãre zuwa ga jama'a mafi ɗaukaka (Malã'iku) ba, kuma anã jĩfar su daga kõwane gẽfe
  9. Dõmin tunkuɗẽwa kuma sunã da wata azãba tabbatacciya
  10. Fãce wanda ya fizgi wata kalma, sai yũla mai haske ta bĩ shi
  11. Ka tambaye su: "Shin sũ ne mafi wuya ga halittawa, kõ, kuwa waɗanda Muka halitta?" Lalle Mũ, Mun halitta su daga lãkã mai ɗauri
  12. Ã'a, kã yi mãmãki, alhãli kuwa sunã ta yin izgili
  13. Kuma idan aka tunãtar da su, bã su tunãwa
  14. Idan suka ga wata ãyã, sai su dinga yin izgili
  15. Kuma su ce, "Wannnan bã kõme ba, fãce sihiri, ne bayyananne
  16. Shin, idan mun mutu, kuma muka kasance turɓaya da kasũsuwa, ashe, lalle mũ tabbas waɗandaake tãyarwa ne
  17. Ashe kõ da ubanninmu na farko
  18. Ka ce: "Na'am alhãli kuwa kunã ƙasƙantattu
  19. Tsãwa guda kawai ce, sai gã su, sunã dũbi
  20. Kuma su ce: "Yã bonenmu! Wannan ita ce rãnar sakamako
  21. Wannan ita ce rãnar rarrabẽwa wadda kuka kasance kuna ƙaryatãwa
  22. Ku tãra waɗanda suka yi zãlunci, da abõkan haɗinsu, da abin da suka kasance sunã bautãwa
  23. Wanin Allah, sabõda haka ku shiryar da su zuwa ga hanyar Jahĩm
  24. Kuma ku tsayar da su, lalle su, waɗanda ake yi wa tambaya ne
  25. Me ya sãme ku, bã ku taimakon jũna
  26. Ã'a, sũ a yau, mãsu sallamãwa ne
  27. Kuma sãshensu ya fuskanta ga sãshe, sunã tambayar jũna
  28. Suka ce: "Lalle kũ, kun kasance kunã jẽ mana daga wajen dãma (inda muka amince)
  29. Suka ce: "Ã'a, ba ku kasance mũminai ba
  30. Kuma wani dalĩli bai kasance ba gare mu a kanku. Ã'a, kun kasance mutãne ne mãsu kẽtare iyãka
  31. Sabõda haka maganar Ubangijinmu ta wajaba a kanmu. Lalle mũ, mãsu ɗanɗanãwa ne
  32. Sabõda haka muka ɓatar da ku. Lalle mũ, mun kasance ɓatattu
  33. To lalle sũ a rãnar nan, mãsu tãrayya ne a cikin azãbar
  34. Lalle Mũ, kamar haka Muke aikatãwa game, da mãsu laifi
  35. Lalle sũ, sun kasance idan an ce musu: "Bãbu abin bautãwa, fãce Allah," sai su dõra girman kai
  36. Kuma sunã cẽwa, "Shin, mũ lalle mãsu barin gumãkanmu ne, sabõda maganar wani mawãƙi mahaukaci
  37. Ã'a, yã zo da gaskiya kuma ya gaskata Manzanni
  38. Lalle kũ, haƙĩƙa mãsu ɗanɗana azãba mai raɗaɗi ne
  39. Kuma bã zã a sãka muku ba fãce da abin da kuka kasance kunã aikatãwa
  40. Fãce bãyin Allah waɗanda aka tsarkake
  41. Waɗannan sunã da abinci sananne
  42. Ya'yan itãcen marmari, kuma sunã waɗanda ake girmamãwa
  43. A cikin gidãjen Aljannar ni'ima
  44. A kan karagu, sunã mãsu fuskantar jũna
  45. Anã kẽwayãwa a kansu da hinjãlan giya, ta daga waɗansu marẽmari
  46. Farã mai dãɗi ga mashãyan
  47. A cikinta bãbu jirĩ kuma ba su zama mãsu mãye daga gare ta ba
  48. Kuma a wurinsu, akwai mãtan aure mãsu taƙaita kallonsu, mãsu manyan idãnu
  49. Kamar dai su ƙwai ne ɓõyayye
  50. Sai sãshensu ya fuskanta a kan sãshe, sunã tambayar jũna
  51. Wani mai magana daga cikinsu ya ce: "Lalle ni wani abõki ya kasance a gare ni (a dũniya)
  52. Yanã cewa, "Shin, kai lalle, kanã daga mãsu gaskatãwa ne
  53. Ashe, idan muka mutu, kuma muka, kasance turɓaya da kasũsuwa, ashe, lalle, mũ tabbas waɗanda ake sãka wa ne
  54. (Mai maganar) ya ce: "Shin, kõ ku, mãsu tsinkãya ne (mu gan shi)
  55. Sai ya tsinkãya, sai ya gan shi a cikin tsakar Jahim
  56. Ya ce (masa), "Wallahi, lalle, kã yi kusa, haƙĩƙã, ka halakãni
  57. Kuma bã dõmin ni'imar Ubangijĩna ba, lalle, dã na kasance daga waɗanda ake halartarwa (tãre da kai a cikin wutã)
  58. Shin fa, ba mu zama mãsu mutuwa ba
  59. Sai mutuwarmu ta farko, kuma ba mu zama waɗanda ake azabtarwa ba
  60. Lalle, wannan shĩ ne babban rabo mai girma
  61. Sabõda irin wannan, sai mãsu aiki su yi ta aikatãwa
  62. Shin wancan shĩ ne mafi zama alhẽri ga liyafa kõ itãciyar zaƙƙũm
  63. Lalle, Mũ, Mun sanya ta fitina ga. azzãlumai
  64. Lalle ita wata itãciya ce wadda take fita daga asalin Jahĩm
  65. Gundarta, kamar dai shi kãnun Shaiɗan ne
  66. To, lalle sũ haƙĩƙa mãsu ci ne daga gare ta. Sa'an nan mãsu cika cikuna ne daga gare ta
  67. Sa'an nan lalle sunã da wani garwaye a kanta, daga ruwan zãfi
  68. Sa'an nan lalle makomarsu, haƙĩƙa, zuwa ga Jãhĩm take
  69. Lalle sũ, sun iske ubanninsu batattu
  70. Sabõda haka sũ, a kan gurãbunsu, suke gaggãwa
  71. Kuma tabbas haƙĩƙa mafi yawan mutãnen farko sun ɓace a gabãninsu
  72. Kuma tabbas haƙĩƙa, Mun aika mãsu gargaɗi a cikinsu
  73. Sai ka dũba yadda ãƙibar waɗanda aka yi wa gargaɗi ta kasance
  74. Fãce bãyin Allah waɗanda aka tsarkake
  75. Kuma lalle, haƙĩƙa' Nũhu ya kira Mu. To, madalla da mãsu karɓãwa, Mu
  76. Kuma Mun tsĩrar da shi da mutãnensa daga bakin ciki babba
  77. Muka sanya zurriyarsa sunã mãsu wanzuwa
  78. Kuma Muka bar masa (yabo) a cikin jama'ar ƙarshe
  79. Aminci ya tabbata ga Nũhu, a cikin halittu
  80. Lalle Mũ kamar haka Muke sãka wa mãsu kyautatãwa
  81. Lalle shi, yanã daga bãyin Mu mũminai
  82. Sã'an nan Muka nutsar da waɗansunsu
  83. Kuma lalle daga ƙungiyarsa, haƙĩƙa, Ibrahĩm yake
  84. A lõkacin da ya je wa ubangijinsa da zũciya kuɓutacciya
  85. A lõkacin da ya ce wa ubansa da mutãnensa, "Mẽne ne kuke bautãwa
  86. Shin, ƙiren ƙarya (wãtau) gumãka, wanin Allah, kuke bautãwa
  87. To, mẽne ne zatonku game da Ubangijin halittu
  88. Sai ya yi dũbi, dũba ta sõsai, a cikin taurãri
  89. Sã'an nan ya ce: "Nĩ mai rashin lãfiya ne
  90. Sai suka jũya ga barinsa, sunã mãsu jũyãwa da bãya
  91. Sai ya karkata zuwa ga gumãkansu, sa'an nan ya ce: "Ashe bã zã ku ci ba
  92. Me ya sãme ku, bã ku magana
  93. Sai ya zuba dũka a kansu da hannun dãma
  94. Sai suka fuskanto zuwa gare shi, sunã gaggãwa
  95. Ya ce, "Kunã bauta wa abin da kuke sassaƙawa
  96. Alhãli, Allah ne Ya halitta ku game da abin da kuke aikatãwa
  97. Suka ce: "Ku gina wani gini sabõda shi, sa'an nan ku jẽfa shi a cikin Jahĩm
  98. Sabõda haka suka yi nufin makĩda game da shi. Sai Muka sanya su, sũ ne mafi ƙasƙanci
  99. Kuma (Ibrahĩm] ya ce: "Lalle, nĩ mai tafiya ne zuwa ga Ubangijĩna, zai shiryar da ni
  100. Ya Ubangijĩna! Ka bã ni (abõkin zama) daga sãlihan mutãne
  101. Sai Muka yi masa bushãra da wani yãro *mai haƙuri
  102. To, a lõkacin da ya isa aiki tãre da shi, ya ce: "Ya ƙaramin ɗãna! Lalle ne inã gani, a ciki barci, lalle inã yanka ka. To, ka dũba mẽ ka gani?" (Yãron) ya ce: "Ya, Bãbãna! Ka aikata abin da aka umurce ka, zã ka sãme ni, in Allah Ya so, daga mãsu haƙuri
  103. Yayin da suka mika wuya sai muka fansheshi da Rago
  104. Kuma Muka kira shi cẽwa "Ya Ibrahĩm
  105. Haƙĩƙa kã gaskata mafarkin." Lalle kamar haka Muke sãka wa mãsu kyautatãwa
  106. Lalle wannan ita ce jarrabãwa bayyananna
  107. Kuma Muka yi fansar yãron da wani abin yanka, mai girma
  108. Kuma Muka bar (yabo) a kansa a cikin mutãnen ƙarshe
  109. Aminci ya tabbata ga Ibrãhĩm
  110. Kamar haka Muke sãka wa mãsu kyautatãwa
  111. Lalle shĩ, yanã daga bãyinMu mũminai
  112. Kuma Muka yi masa bushãra* Da Is'hãƙa ya zama Annabi daga sãlihan mutãne
  113. Kuma Muka yi albarka a gare shi, kuma ga Is'hãka. Kuma daga cikin zurriyarsu akwai mai kyautatãwa da kuma maizãlunci dõmin kansa, mai bayyanãwa (ga zãluncin)
  114. Kuma lalle, Mun yi ni'ima ga Mũsã da Hãrũna
  115. Kuma Muka tsĩrar da su da mutãnensu daga bakin ciki mai girma
  116. Kuma Muka taimake su, sabõda haka suka kasance mãsu rinjãya
  117. Kuma Muka ba su Littãfi mai iyãkar bayãni
  118. Kuma Muka shiryar da su ga hanya mĩƙaƙƙiya
  119. Kuma Muka bar (yabo) a gare su a cikin mutãnen karshe
  120. Aminci ya tabbata ga Mũsã da Hãruna
  121. Lalle kamar haka Muke sãka wa mãsu kyautatãwa
  122. Lalle, sunã daga bãyin Mu mũminai
  123. Kuma lalle Ilyãs, haƙĩƙa, yanã daga Manzanni
  124. A lõkacin da yake ce wa mutãnensa, "Ashe, bã zã ku yi taƙawa ba
  125. Shin, kunã bauta wa Ba'al ne, kuma kunã barin Mafi kyautatãwar mãsu halitta
  126. Allah Ubangijinku, kuma Ubangijin ubanninku farko
  127. Sai suka ƙaryata shi. Sabõda haka sũ lalle waɗanda zã a halartãwa ne (a wutã)
  128. Sai bãyin Allah waɗanda aka tsarkake
  129. Kuma Muka bar (yabo) a gare shi, a cikin mutãnen ƙarshe
  130. Aminci ya tabbata ga Ilyãs
  131. Lalle Mũ kamar haka Muke sãka wa mãsu kyautatãwa
  132. Lalle shĩ, yanã daga bãyin Mu mũminai
  133. Kuma lalle Lũdu, haƙĩƙa, yanã daga Manzanni
  134. A lõkacin da Muka tsĩrar da shi, da mutãnensa gabã ɗaya
  135. Sai wata tsõhuwa tanã a cikin mãsu wanzuwa (a cikin azãba)
  136. Sã'an nan Muka darkãke waɗansu mutãnen
  137. Kuma lalle kũ, haƙĩƙa, kunã shũɗewa a kansu, kunã mãsu asubanci
  138. Kuma da dare. Shin fa, bã zã ku hankalta ba
  139. Kuma lalle Yũnusa, haƙĩƙa, yanã daga Manzanni
  140. A lõkacin da ya gudu zuwa ga jirgin ruwa wanda aka yi wa lõdi
  141. Sã'an nan ya yi ƙuri'a, sai ya kasance a cikin waɗanda aka rinjaya
  142. Sai kĩfi ya yi lõma da shi, alhãli kuwa yanã wanda ake zargi
  143. To, ba dõmin lalle shi ya kasance daga mãsu tasbĩhi ba
  144. Lalle dã ya zauna a cikin cikinsa har ya zuwa rãnar da zã a tãyar da su
  145. Sai Muka jẽfa shi ga wani fĩli alhãli kuwa yanã mai raunin rashin lãfiya
  146. Kuma Muka tsirar da wata itãciya ta kankana a kusa da shi
  147. Kuma Muka aika shi zuwa ga waɗansu mutãne dubuɗari, kõ sunã ƙaruwa (a kan haka)
  148. Sai suka yi ĩmãni sabõda haka Muka jiyar da su dãdi har wani lõkaci
  149. Sabõda haka, ka tambaye su, "Shin, Ubangijinka ne da 'ya'ya mãtã, kuma su da ɗiya maza
  150. Kõ kuma Mun halitta malã'iku mãtã ne, alhãli kuwa sũ sunãhalarce
  151. To! Lalle sũ, daga ƙiren ƙaryarsu sunã cẽwa
  152. Allah Yã haihu," alhãli kuwa lalle sũ, haƙĩƙa maƙaryata ne
  153. Shin, Yã zãɓi 'yã'ya mãtã ne a kan ɗiya maza
  154. Mẽ ya same ku? Yãya kuke hukuntãwa (wannan hukunci)
  155. Shin, bã ku tunãni
  156. Ko kuma kunã da wani dalĩli bayyananne ne
  157. To, ku zo da littãfinku idan kun kasance mãsu gaskiya
  158. Kuma suka sanya nasaba a tsakãnin Sa da tsakãnin aljannu. Alhãli kuwa Lalle aljannu sun sani, "Lalle sũ, haƙĩƙa waɗanda ake halartarwa ne (a cikin wutã)
  159. Tsarki ya tabbata ga Allah daga abin da suke siffantãwa
  160. Sai bãyin Allah waɗanda aka tsarkake
  161. To, lalle, ku da abin da kuke bautãwa
  162. Ba ku zama mãsu buwãya ba a gare Shi
  163. Sai wanda yake mai shiga babbar wutã Jahĩm
  164. Kuma bãbu kõwa daga cikinmu,* fãce yanã da matsayi sananne
  165. Kuma lalle mu, haƙĩƙa, mũ ne mãsu yin sahu-sahu (dõmin ibãda)
  166. Kuma lalle mũ haƙĩƙa, mũ ne mãsu yin tasbĩhi
  167. Kuma lalle sũ, sun kasance sunã cẽwa
  168. Dã lalle munã da wani littãfi irin na mutãnen farko
  169. Lalle dã mun kasance bãyin Allah waɗanda aka tsarkake
  170. Sai suka kãfirta da shi. Sabõda haka zã su sani
  171. Kuma lalle, haƙĩƙa kalmar Mu ta gabãta ga bãyinMu, Manzanni
  172. Lalle sũ, haƙĩƙa, sũ ne waɗanda ake taimako
  173. Kuma lalle rundunarMu, haƙĩƙa, sũ ne marinjaya
  174. Sabõda haka juya daga barinsu, har a wani lõkaci
  175. Ka nũna musu (gaskiya), da haka zã su dinga gani
  176. Shin fa, da azabarMu suke nẽman gaggãwa
  177. To, idan ta sauka ga farfãjiyarsu, to, sãfiyar wadanda ake yi wa gargaɗi ta mũnana
  178. Kuma ka jũya daga barinsu har a wani lõkaci
  179. Ka nũna (musu gaskiya), da haka zã su dinga nũnãwa
  180. Tsarki ya tabbata ga Ubangijinka, Ubangijin rinjãye, daga barin abin da suke siffantãwa
  181. Kuma aminci ya tabbata ga Manzanni
  182. Kuma gõdiya ta tabbata ga Allah Ubangijin halittu